Home Uncategorized Ramadan: Sarkin Musulmi ya sanar da ganin watan Sha’aban

Ramadan: Sarkin Musulmi ya sanar da ganin watan Sha’aban

8
0

Sarkin Musulmi Alhaji Muhammd Sa’ad Abubakar ya sanar da ganin watan Sha’aban in da ya ayyana yau Lahadi 11 ga watan Fabarairu ta zama 1 ga watan Sha’aban 1445.

Sarkin musulmi y aba da sanarwar ne ga manema labarai a wata takarda da wazirin Sakkwato kuma shugaban kwamitin harkokin addini a majalisar sarkin musulmi Farfesa Sambo Wali Junaid ya sanyawa hannu, hakan ke nuna watan Ramadan zai zo nan da kwana 30.

Da yawan musulmi musamman a Nijeriya suna fatar ganin watan Ramadan ya zo cikin saukin rayuwa ganin yadda tsadar rayuwa ke kara ta’azara a kasar abinci ya gagari talaka.

Malaman addini sun fata wa’azi ga masu hali su taimaki talakawa don samun saukin rayuwar yau da kullum.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here