Najeriya ta rage wa asibitocin gwamnati kashi 50 cikin ɗari na kuɗin wuta

Najeriya ta rage wa asibitocin gwamnati kashi 50 cikin ɗari na kuɗin wuta

Ƙaramin ministan Lafiya a Najeriya, Dakta Tunji Alausa ya sanar da cewa Gwamnatin Tarayya ta amince da bayar da tallafin kashi 50 cikin ɗari na kuɗin wutar lantarki ga asibitocin gwamnati a faɗin ƙasar.

A cewarsa, an yi hakan ne domin rage kuɗaden da ake kashewa wajen gudanar da asibitoci, da kuma rage wahalar da masu jinya suke sha.

Ministan ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyara asibitin Ƙwaƙwalwa da ke Barnawa a Kaduna domin ƙaddamar da fasahar adana bayanai da injin samar da lantarki (jannareto) a ɗakin aikin gaggawa na asibitin.

Haka kuma an mayar da ɗakin wankin ƙoda mai amfani da hasken rana.