Mutum Biyu Sun Rasu Daya ya samu Rauni A Hadarin Mota A Neja

Mutum Biyu Sun Rasu Daya ya samu Rauni A Hadarin Mota A Neja
Mutum Biyu Sun Rasu Daya ya samu Rauni A Hadarin Mota A Neja
Hukumar kiyaye hadurra ta jihar Neja ta ce mutum biyu ne suka rasu a hadarin mota da auku a kan hanyar Kutigi-Mokwa a ranar Lahadi.
Kwamandan hukumar Musa Muhammad ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai a garin Minna ya ce dayan mutum ya samu rauni a hadarin.
"Mutum uku ne suka fada a hadarin in da mutum biyu suka kone abin da ya sa suka rasa ransu dayan kuwa ya samu rauni" a cewarsa
Ya ce hadarin ya auku ne da babbar motar Dangote da kuma DAF wadda take ta NNPC ce a kauyen Edati.