Matsalar Tsaro:Kungiyoyin Matasa Masu Kishin Sakkwato Sun Yi Karatun Kur'ani 

Matsalar Tsaro:Kungiyoyin Matasa Masu Kishin Sakkwato Sun Yi Karatun Kur'ani 
Matsalar Tsaro:Kungiyoyin Matasa Masu Kishin Sakkwato Sun Yi Karatun Kur'ani 
Kungiyoyin Matasa masu  kishin jahar Sakkwato sun halllara a Masallacin Sarkin Musulmi Abubakar III da yammacin  Lahadi  bayan Sallah La'asar suka yi  Karatun Alqur'an Maigirma bayan an  kammala  aka yi Addu'o'i na Musamman da rokon Allah domin Samun saukin wadannan fittinun da suke faruwa a Jahar na Kashe kashen Jama'a.   
 Ayankunan Sabon Birni, Isa, Rabah, Goronyo,Wurno da Sauran sassan kasar nan Nijeriya zubar da jini ya zama ruwan dare. 
Matasan sunyi kira ga mahukunta da su yi gaugawar daukar matakin akan wannan Matsalar da ta addabi mutane ta hana kwanciyar hankali a cikin al'umma.
      Daga M  A FARUK SOKOTO