Matasa sun nemi Bafarawa ya dawo cikin harkar siyasa

Matasa sun nemi Bafarawa ya dawo cikin harkar siyasa

Matasa masu kishin tafiyar siyasar tsohon Gwamnan Sakkwato Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa sun nemi da ya dawo harkar siyasa gadan-gadan bayan ya sanar da jingine siyasa da ya yi a lokuttan da suka gabata.
Matasan da suka taru a gidan Bafarawa don su roke shi ya sake dawowa cikin harkokin siyasa ba kamar yadda ya kudurta a farko ba, sun ce siyasar Sakkwato ba ta inganta in ya cire hannunsa cikinta.
Alhaji Babangida amadadin matasa ya zayyano muhimmanci Bafarawa a siyasar Sakkwato Wanda hakan zai sa su magoya bayansa ba za su lamunce ya cire hannunsa a harkokin siyasa ba.
Tsohon Gwamna Bafarawa a jawabin da ya yi wa magoya bayansa kan bukatar su, ya sanar yanda yake rayuwa tun bayan barin mulki a cikin dogara da Allah hakan yake so magoya bayansa su kasance komai abarwa Allah, amma dai a tashi a yi aiki don cigaba a jihar Sakkwato.
In ba a manta ba tsohon Gwamnan ya sanar cewa ya yi ritaya a siyasa abin da ya haifar da cece ku ce a jiha ganin wannan maganar wani abu ne mai wahalar gaske tsohon Gwamna ya jingine siyasa.