Mataimakin Gwamnan Jihar Sakkwato Ya Bar Jam'iyar PDP

Mataimakin Gwamnan Jihar Sakkwato Ya Bar Jam'iyar PDP

Mataimakin Gwamnan jihar Sakkwato Honarabul Manir Muhammad Dan'iya ya bar jam'iyarsa ta PDP.
Barin jam'iyar ya fito a wata takardar da ya sanyawa hannu dake yawo a kafafen sadarwa na zamani wadda ya aika ga shugaban mazabarsa ta Kware a karamar hukumar Kware a jihar Sakkwato.
A takardar Mataimakin Gwamna ya sanar cewa ya janye shedar zamansa dan jam'iyar PDP tun da 8 ga watan Fabarairu na 2023.
Ya godewa damar da aka ba shi ya yi aiki matakai da dama a cikin jam'iyar PDP.
Darakta yada labarai a ofishin mataimakin gwamnan Aminu Abdullahi bai dauki wayarmu ba domin sanin sahihancin takardar.