Mataimakin Gwamna Ne  Na Hadu A Cikin Jerin Masu Son PDP Ta Tsayar Da Su Takarar Gwaman Sakkwato

Mataimakin Gwamna Ne  Na Hadu A Cikin Jerin Masu Son PDP Ta Tsayar Da Su Takarar Gwaman Sakkwato

 

Mataimakin Gwamnan Jihar Sokoto Honarabul  Manir Muhammad Dan'iya,  ya Saye Form na bayyana aniyarsa ta takarar  Gwamnan Jihar Sokoto a Zaben kasa na 2023 cikin jam'iyar PDP zuwa yanzu shi ne mutum na hudu. 

 

Alhaji Murtala Dan’iya tare da Rakiyar Usman El-Kudan da Barista Adah ne suka amso masa form din a Ofishin Uwar Jamiyar PDP dake Abuja.  
 

Mataimakin Gwamnan ya yi  godiya ga Gwamna  Aminu Waziri Tambuwal akan  dama da ya bashi na taya shi jagorancin Jihar Sokoto, kuma yana neman Adduoi da samun nasara a  sabuwar tafiya.