Masu Zanga Zanga Sun ci Karfin Jami’an Tsaro, an Toshe Babbar Hanyar Abuja Zuwa Kaduna

Masu Zanga Zanga Sun ci Karfin Jami’an Tsaro, an Toshe Babbar Hanyar Abuja Zuwa Kaduna


"Da misalin karfe 10 na safiyar yau Alhamis motarmu ta bar garin Zuba inda matasa masu anga-zanga suka toshe hanya a dai dai kwanar Gauraka. 
"Mun shafe awanni biyu muna tsaya waje daya, matasan sun mamaye titin gaba daya, kuma an samu cunkoson ababen hawa tsakanin kauyen Aluminum da barikin soji na Zuma." 
Abubakar Ibrahim ya ce akwai wasu jami'an 'yan sanda da ke nesa kadan da wajen, amma sun gaza yin komai domin nemanwa matafiya hanyar wucewa. "
"Akwai 'yan sanda kadan da ke tsaye daga nesa, amma ba za su iya yin komai ba game da tsohe hanyar saboda yawan matasan ya fi karfinsu." - Inji Abubakar. 
Daruruwan matafiya ne a halin yanzu suka makale a kan titin Suleja wanda ke kan babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna a jihar Neja. Hakan ya faru ne a sakamakon hana zirga-zirgar ababen hawa a wani sashe na hanyar da masu zanga-zangar yunwa suka yi.