Managarciya Na Neman Marubuta

Managarciya Na Neman Marubuta

Managarciya Na Neman Marubuta

Amadadin hukumar gudanarwa ta kafar yada labarai mai suna MANAGARCIYA na bukatar gudunmuwar marubuta domin kara ciyar da al’umma a gaba.

Managarciya na bukatar rubutun makala kan wani maudu’i da marubuci ya zaba domin ilmanatarwa da fadakarwa a cikin al’umma.

A duk makala daya akwai dan hasafi na naira 1000 don sanya kati da za a baiwa marubuci bayan cika sharudda kamar haka:

  • Sai mutum 500 sun bude makalar marubuci,
  • Sai an samu share 20 na makalar,
  • Ana bukatar Comment 20 na mutane daban-daban,
  • Sai an samu like na mutum 10 a makalar.

Duk marubucin da ya aminta da hakan zai iya turo makalarsa ta wannan adireshi: managarciya@gmail.com zai kuma turo email da za a yi masa rijista a saman web na Managarciya domin bibiyar sakamakon sharudda da wallafa wasu rubutu da yake bukata.

Mun gode,

Edita.