Mahajjaciyar Nijeriya Ta Rasu A Filin Arfa

Mahajjaciyar Nijeriya Ta Rasu A Filin Arfa

Allah ya yi wa wata mahajjaciyar Nijeriya, ƴar jihar Kaduna rasuwa a yau Juma'a a filin Arafat da ke birnin Makkah.

Rahotanni sun bayyana cewa, mahajjaciyar, mai suna Hasiya Aminu,  daga Ƙaramar Hukumar Zariya a ta rasu ne a filin Arafat jim kaɗan bayan ta gama taimakawa wajen rabon abinci ga alhazai a tantinsu da ke filin na Arafa.

Da ya ke tabbatar da rasuwarta, muƙaddashin Daraktan Ayyuka na  Hukumar Jin daɗin Alhazai ta Jihar Kaduna,  Abubakar Alhassan ya ce a safiyar yau marigayiyar na daga cikin alhazan da su ka je Jabbal Rahma (dutsen rahama) da ke filin Arfa.

Yace ta rasu a cikin tanti ba tare da wani ciwo ba.