Home Uncategorized Kwamitin bincike na gwamnatin Sokoto ya baiwa Manir Dan’iya da Yusuf Suleiman...

Kwamitin bincike na gwamnatin Sokoto ya baiwa Manir Dan’iya da Yusuf Suleiman dama ta ƙarshe

2
0

Kwamitin bincike da gwamnatin Sakkwato ta kafa ya  gargaɗi tsohon mataimakin gwamna Alhaji Manir Muhammad Dan’iya a karo na karshe  da ya  bayyana a gabanta  a zaman da za ta sake yi 22 ga watan Mayun 2024.

Haka ma kwamitin ya tura irin wannan gargadin ga tsohon babban daraktan kamfen jam’iyar PDP a zaben 2023 Alhaji Yusuf Suleiman Ɗan Amar Sokoto.

A cewar kwamitin dukkan su biyu akwai bayanin da ake so su yi a gaban kwamitin kan wani Memo 007  da ke gaban kwamitin.

Lauya Dan’iya, Barista Nuhu Adamu ya nemi a sanya masu wata rana abin da shugaban MU’AZU Pindiga   ya aminta da hakan.

Ya umarci ‘yan sanda su lika takardar gayyata a jikin ginar Dan’amar Sokoto in har ba a same shi gida ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here