Kotu Ta Tabbatar Da Zaben Gwamnan Sakkwato Ahmad Aliyu

Kotu Ta Tabbatar Da Zaben Gwamnan Sakkwato Ahmad Aliyu
 
 
Kotun sauraren korafin zaben 2023 wadda ta zauna domin jin bahasin kalubalantar zaben Gwamnan jihar Sakkwato Alhaji Ahmad Aliyu da mataimakinsa Idris Muhammad Gobir in da dan takarar Gwamna a jam'iyar PDP Alhaji Sa'idu Umar na jam'iyar PDP ya shigar ta yi watsi da Karar dake gabanta.
Mai Karar Sa'idu Umar ya kalubalanci zaben Ahmad Aliyu na jam''iyar APC kan rashin cancanta da Kuma tabka aringizon kuri'u a zaben Gwamna da aka yi 18 ga watan Maris na 2023.

A hukuncin da alkalan uku  suka gabatar dukansu sun amince da magana guda jagoransu Haruna Mishelia ya ce masu Kara sun kasa tabbatar da zarge-zarge shidda suke kalubanta a gaban kotu. 

Ya ce korafin masu Kara kan zargin Ahmad Aliyu da Gobir bai kamata su yi takarar ba domin sun gabatar da takardun bugi, ga matsalar suna da magudin zabe da Kuma sabawa dokokin zabe.

Mshelia ya ce masu Karar sun kasa tabbatar da abubuwan da suke korafi kansu kamar yadda doka ta tanadar Kashi 70 na shedun da suka gabatar ba su shafi Karar ba lamari ne da ya shafi zaben majalisar dokokin jiha Wanda a rana daya aka gudanar da zaben.

Alkalin ya yi watsi da Karar domin rashin cancantarta a tsarin doka.