Kotu Ta Tabbatar Da Nasarar ‘Yan Majalisar Tarayya 4 Na PDP a Sokoto

Kotu Ta Tabbatar Da Nasarar ‘Yan Majalisar Tarayya 4 Na PDP a Sokoto

Kotun daukaka kara dake zama a Abuja ta tabbatar da nasarar ‘yan majalisar wakillai 4 da suka fito daga jam’iyar PDP a jihar Sakkwato.

Jam’iyar PDP ta taya murna ga ‘yan majalisar kan nasarar da suka samu a kotun daukaka kara in da ta roke su da su cigaba da aiki tukuru domin samun nasarar jam’iyar  a fannoni daban-daban.

'Yan majalisar da suka samu nasara sun hada da Honarabul  Mani Maishinko Katami, mai wakiltar kananan hukumomin Binji da Silame da  Honarabul  Abdussamad Dasuki a Kebbe da  Tambuwal da Honarabul  Sa'idu Bargaja a Isa da  Sabon-Birni da Honaraul  Bashir Mohammed Gorau a  Goronyo da Gada.

A sanarwar da jami'in yada labarai na PDP a jiha Hassan Sahabi Sanyinnawal ya fitar ya taya murna ga wadan da suka samu nasara da jam'iyar PDP gaba daya.