Karancin Naira: Matasa Masu  Zanga-Zanga Sun Kai Hari Ofishin Gwamna

Karancin Naira: Matasa Masu  Zanga-Zanga Sun Kai Hari Ofishin Gwamna

 

Mumunar zanga-zanga ta barke a Ibadan, babbar birnin jihar Oyo sakamakon halin kunci, tsadar kaya, da kuma rashin takardun Nairan siya ko abinci a Najeriya. 

Hotuna da bidiyoyi sun nuna yadda fusatattun matasa sun tare hanyoyi suna kone-konen tayoyi. 
TheNation ta ruwaito cewa matasan sun kai hari ofishin gwamnan jihar, Seyi Makinde. 
Har direbobin motocin haya ba'a bari a baya ba wajen zanga-zangar. 
Halin da talaka ya shiga kan karancin man fetur da naira akwai bukatar gwamnati ta yi wani abu cikin gagggawa.