Kakakin majalisar Sakkwato ya ƙauracewa zaɓen shugabanin APC
Ya ce "Mun amince Sakkwato za mu yi zabe babu hamayya waton na amincewa, amma ba mu hana wanda yake son ya shiga zabe ya fito ba sai a gudanar da zabe wanda ya samu nasara shi ne na jama'a." a cewarsa. Shugaban kwamitin gudanar da zaɓen a jihar Sakkwao Abubakar Suleman Iyan Akko a jawabinsa ga jagororin jam'iya ya ce sun zo ne amadadin hidikwatar APC don gudanar da zaben shugabanni kuma sun gamsu da tsarin da suka tarar.
Isah Sadik Achida ya yi wa kwamitin zaben barka da zuwa amadadin masu ruwa da tsaki na jam'iyar.
managarciya