Jirgin Sojin Najeriya Ya Kai Sabon Samame Mafakar Bello Turji, Su Kuma Maharan Sun Tare Hanyar Sakkwato Zuwa Gusau

Jirgin Sojin Najeriya Ya Kai Sabon Samame Mafakar Bello Turji, Su Kuma Maharan Sun Tare Hanyar Sakkwato Zuwa Gusau

 

Jirgin yaƙin rundunar sojin saman Najeriya (NAF) ya kai sabon hari sansanin ƙasurgumin ɗan bindigan nan, Bello Turji, a jihar Zamfara. Daily Trust ta ruwaito cewa ƙasurgumin ɗan ta'addan ya tsallake rijiya da baya a wani harin ruwan bama-bamai da sojoji suka kaddamar a gidansa ranar Asabar. 

Wata majiya ya shaida mana cewa Jirgin ya sake koma wa wurin da misalin ƙarfe 9:00 na safiyar yau Litinin, ya saki aƙalla bama-bamai guda biyu. 
Legit.ng Hausa ta tattaro cewa a kwanakin baya, gwamnatin Zamfara ta yi ikirarin cewa Bello Turji, ya rungumi shirin zaman lafiya da gwamnatin Matawalle ta zo da shi. 
A halin yanzun, wasu 'yan bindigan daji da ake kyautata zaton mayaƙan Bello Turji ne sun kai hari kan matafiya a babban titin Sakkwato zuwa Gusau, a ƙaramar hukumar Shinkafi. 
Wani mazaunin garin Shinkafi, Murtala Wadatau, yace yan ta'addan sun tsohe hanya a Kwanar Badarawa da Birnin Yero da safiyar Litinin ɗin nan. 
Wannan na zuwa ne a dai-dai lokacin da gwamnati ta yi ikirarin cewa ta samu galaba kan taɓarɓarewar tsaron da aka sha fama da shi a sassan Najeriya. Gwamnatin ta bakin ministan yaɗa labarai, Lai Muhammed, tace duk da akwai sauran yaƙi, amma sojoji sun samu nasarori da dama kan 'yan ta'adda.