Home Uncategorized Gwamnan Sokoto ya ba da goron sallah ga dukkan ma’aikatan jiha

Gwamnan Sokoto ya ba da goron sallah ga dukkan ma’aikatan jiha

7
0
Gwamnan jihar Sakkwato Dakta Ahmad Aliyu Sokoto ya aminta da fitar da kudi domin bayar da goron sallah ga dukkan ma’aikatan jiha da masu karbar fansho da masu karbar alawus a ƙananan hukumomi da hukumar kiyon lafiya matakin farko.
Goron Sallar Gwamna ya raba shi gida biyu, ma’aikatan jiha dana ƙananan hukumomi za a ba su dubu 30 kowanensu.
Masu karbar fansho da alawus dana hukumar lafiya matakin farko za su amfana da dubu 20 suma don shagalin sallah.
Wannan kyautar za a fara biya ne daga 13 ga watan Yuni 2024 a gobe Alhamis kenan kamar yadda sakataren yada labarai na Gwamna ya sanar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here