Gwamna Ahmad Ya Saukar Da Sarakunan Da Tambuwal Ya Naɗa a Sakkwato

Gwamna Ahmad Ya Saukar Da Sarakunan Da Tambuwal Ya Naɗa a Sakkwato

Gwamnan jihar Sakkwato Ahmad Aliyu Sokoto ya saukar da sarakunan da Tambuwal ya naɗa a lokacin mulkinsa.
Sanarwar  dakatarwar nada sahannun mai magana da yawun Gwamna Alhaji Abubakar Bawa in da ya karantawa manema labarai a fadar gwamnatin jiha, ya ce an dakatar da sarakunan da Gwamna Tambuwal ya naɗa a satin da ya gabata kuma za a waiwayi dakatarwa daga baya domin cigaban jama'a.
Bawa ya ce duk filayen da Tambuwal ya bayar a makwanin da suka gabata an soke kyautar.
Ya ce duk wasu kayan gwamnati da aka yi gwanjonsu abin bai yi ba.