Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf a yanzu haka na ganawa da shugaban ƙasa Tinubu a fadar shugaban ƙasa dake Abuja kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.
Gwamnan sanye da jar hula da babbar riga ya isa fadar shugaban ƙasa da karfe 4:10 na yammacin yau.






