Dole Fa Gwamnati Ta Yi Dokokin Aure A ƙasar Hausa— Dakta Mus’ab Isah Mafara

Sannan gwamnati da ƙungiyoyi ma su zaman-kan-su da ma ɗaiɗaikun mutane ya kamata su ɗauki nauyin shirye-shirye a gidajen radiyo da wasu kafafen kamar irin wasan kwaikwayo, ko sanarwowi, ko wa’azi, ko waƙoƙi, ko tallace-tallace, ko wanin su, waɗanda kacokan za a gina su ne a kan illar aurarraki waɗanda ba su da ƙaidi da illar da ke tattare da tara yara ga wanda sam bai da ikon ɗaukar nauyin su. Sannan a gargaɗi iyaye da waliyyai a kan munin ba da diyar su ga irin waɗannan mazajen wai kawai don ka da a ce su na da budurwa a gida sun ƙi yi ma ta aure.

Dole Fa Gwamnati Ta Yi Dokokin Aure A ƙasar Hausa— Dakta Mus’ab Isah Mafara

 

 

 

 

Rubutawa: Dakta Musab Isah Mafara.

 

Ba labaran da ke baƙanta min rai ko yaushe na ziyarto Najeriya irin yadda

bahaushe ke walaƙanta al’amarin iyali. Daga ka ga direba wanda albashi nai

bai kai dubu talatain ba, amma ya na da mata ukku da ɗiya fiye da ishirin

sai ka ji ma’aikacin gwamnati kuma wai ‘mai ilmi’ mai hali amma ya wohintar

da jin-daɗin iyali nai. Wai ya za a yi al’umma ta ci gaba alhali mu na

kallo mazaje matalauta su na aurarraki su na zubo yara ba kan-gado bayan

mun kwan da sanin cewa ba za su iya ɗaukar nauyin yaran nan ba.

Ya za a yi a zuba ido a bar al’umma ta ci-gaba da taɓarɓarewa haka. Sannan ga wasu

‘masoya addini’ ‘yan-birni da yaran su ba su wuce ukku ko hudu ba ga tazara

ta shekara akallau ukku tsakanin yaran amma da ka ce a taƙaita haihuwa da

aure-aure sai su fara kunfan baki wai a na faɗa da addini.

 

Wallahi ba yadda za a yi Musulunci ya umurce mu da irin wanga tara iyali da

mu ke yi a ƙasar Hausa na ba gaira ba sabat. Ka na da albashi da bai kai ya

kawo ba amma wai da ka samu wasu ‘ƴan kuɗin hutu ko kasuwa ta yi kyau sai

ka je ka ƙara aure ka yi ta haihuwa ka sako ma al’umma yara ta san yadda za

ta yi da su. Ga matar ka — ko matan ka — da yaran ka gida su na cikin

wahala amma kai jin-dadin gaban ka kawai shi ka ke kallo ba maslahar iyalin

ka ba. Mu na zaune ba wata doka ko tsari ko al’ada da za ta bincika ta gani

ko mai son ƙara aure ya kai munzalin a bar shi ya ƙara aure ko kuma a’a. Mu

na zaune mu na kallo mutane su na haiho yara su bar su ga titi su na

gararamba, ba su san cin su ko shan su ko wurin kwanan su ba? Yara su zo su

addabi mutanen unguwa da sace-sace da dabanci, ba su ganin girman kowa ba

su jin maganar kowa Kai! Wallahi akwai haɗari!

 

Rashin fahimtar tawakkali ne ka yi ta haihuwa ba tare da ka yi wani tanadi

ma yaran ba kawai kai ka na da tunanin cewa bakin da Allah Ya tsaga to zai

ba shi abun da zai ci. E, za su ci gidan maƙwabta, za su ƙwato, za su sato,

za su barato. Kai kuma ku je lahira Allah Ya yi ma ka hisabi na cin-haƙƙin

yaran da ba su ji ba ba su gani ba. Wai in ba jahilci da son-rai irin na

bahaushe ba ya za a yi ka taƙarƙare kan sunnar aure ka watsar da farilla ta

takalihun iyali. Kai bagidajen ina ne! An san Allah Ya na talauta attajiri

ya azurta talakka amma mazon Allah (SAW) ma cewa ya yi wanda ke da HALI ya

yi aure. Wallahi irin bala’in da ke fuskantar ‘kasar Hausa — ba fata ni ke

yi ba — ya dama matsalar boko-haram da bandits ya shanye in a ka ci-gaba da

tafiya haka .

 

Dole fa gwamnati ta yi dokoki na aure a ƙasar Hausa kwatankwacin waɗanda

Maigirma Sarki Sanusi II ya nemi da a yi can baya. Na san ba mutane mu ke

ma su bin doka ba kuma gwamnatocin mu ko dokar da za ta kawo mu su ƙarin

kuɗin-shiga ba su tabbatar ba balle doka ta inganta zamantakewar al’umma.

Duk da haka dai mu na roƙon gwamnatocin arewa da su yi dokokin su kuma yi

ƙoƙari na tabbatar da su. A kuma ba al’umma ilmi gwargwadon hali saboda

duhun jahilci ke sa wasu mutanen ke gudanar da rayuwar su ta iyali kamar

dabbobi. Sannan mu na roƙon malaman mu da su wa Allah su gargaɗi mutane a

kan illar tara mata da zubo yara ga wanda bai da abun takalihun su. Mutanen

mu su na girmama magana in a ka biyo da ita ta addini. A nuna mu su irin

haƙƙin da Allah Ya aza mu su na kula da mata da yaran su.

 

Sannan gwamnati da ƙungiyoyi ma su zaman-kan-su da ma ɗaiɗaikun mutane ya

kamata su ɗauki nauyin shirye-shirye a gidajen radiyo da wasu kafafen kamar

irin wasan kwaikwayo, ko sanarwowi, ko wa’azi, ko waƙoƙi, ko

tallace-tallace, ko wanin su, waɗanda kacokan za a gina su ne a kan illar

aurarraki waɗanda ba su da ƙaidi da illar da ke tattare da tara yara ga

wanda sam bai da ikon ɗaukar nauyin su. Sannan a gargaɗi iyaye da waliyyai

a kan munin ba da diyar su ga irin waɗannan mazajen wai kawai don ka da a

ce su na da budurwa a gida sun ƙi yi ma ta aure.

 

Wallahi dole mu ja daga mu yaƙi wasu mugayen ɗabi’u na alummar mu. Kuma mu

rufe idanu da kunnuwan mu ga duk mai suka da waɗanda za su yi zargin cewa

faɗa da zubo yara barkatai irin na bahaushe kamar faɗa da addini ne. Haba!!!