'Dalilinmu Na Gudanar da Sallah Ba Ranar da Sarkin Musulmi Ya Aiyana ba' 

'Dalilinmu Na Gudanar da Sallah Ba Ranar da Sarkin Musulmi Ya Aiyana ba' 


 

Malamin addinin musulunci Malam Musa Lukuwa ya ki bin umarnin Sarkin Musulmi Alhaji Sa'ad Abubakar ya gudanar da sallah karama tare da mabiyansa a wannan Lahadin sabanin Litinin.

A jiya Assabar Sarkin Musulmi ya sanar cewa watan Shawwal na wannan shekara ta 1443 bai kama ba.
Mabiya malamin sun gudanar da Sallar ne a birnin Sakkwato da karfe Takwas na safe.
A bayaninsa ga manema labarai Lukuwa ya ce ya samu cikakken rahoton ganin jinjirin watan a wasu wurare na Nijeriya da wajenta.
Ya kuma ce ba wata da'a ga kowa wurin saba ubangiji, "duk wanda ya yi azumi a yau ya yini ne da yunwar banza ba wanda ya sa shi domin wata azumi ya wuce" a cewarsa.  

Al'ummar kasar Nijar sun yi sallah a yau Lahadi suma domin wata ya bayyanu a kasarsu.