An Gano Sunayen Mutum 3 da Tinubu Ke Shirin Baiwa Manyan Muƙamai

An Gano Sunayen Mutum 3 da Tinubu Ke Shirin Baiwa Manyan Muƙamai

Rahotannin da ke fitowa a halin yanzu sun nuna cewa zaɓaɓɓen shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, na shirin naɗa kakakin majalisar wakilan tarayya, Femi Gbajabiamila, a babban matsayin da zaran ya karɓi mulki.

Bayanan sun nuna cewa Tinubu na shirin gwangwaje Gbajabiamila da muƙamin shugaban ma'aikatan fadarsa idan aka rantsar da shi ranar Litinin, 29 ga watan Mayu, 2023.
 
Rahoton This Day ya ce, manyan mutane kamar Wale Edun, tsohon kwamishinan kuɗi a jihar Legas da kuma gwamnan jihar Kebbi mai ci, Atiku Bagudu, na cikin jerin sunayen da Tinubu ya ware wa babban muƙami da zai yi a cikin hanzari bayan ya karbi mulki. 
Wasu majiyoyi sun bayyana cewa sunayen Mista Edun da Atiku Bagudu, sun fita a cikin tawagar ɓangaren tattalin arziki a gwamnatin Tinubu yayin da ake tunkarar bikin rantsarwa. 
"Da yuwuwar Wale ne zai zama jagoran bangaren tattalin arziki, ko dai Ministan kuɗi ko kuma gwamnan babban bankin Najeriya (CBN).
Har yanzun bamu da taƙamaiman shirin Tinubu kan Bagudu." "Amma yana cikin waɗanda sunansu ya shiga ciki kuma zai ja ragamar babban ɓangare mai matuƙar muhimmanci a gwamnati mai kama wa."
Idan zaku iya tunawa, Legit.ng ta kawo muku rahoton cewa Gbajabiamila na hanyar zama shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin tarayyan Najeriya na gaba.
Wata majiya ta daban da ta yi tsokaci kan wannan labarin, ta ce: "Idan kuka tuna, bai karɓi shaidar cin zaɓe ba ranar Laraba, ba ya buƙatar Satifiket ɗin INEC, yana da duk abinda ya kamata na aiki a matsayin shugaban ma'aikatan shugaban kasa a sabuwar gwamnati."