Managarciya

Abubuwan Da Ke Kawo Cibaya A Arewacin Nijeriya—Gwamnan Katsina

 

A wani bidiyo da ke yawo a kafofin sada zumunta na zamani, an ji Umaru Dikko Radda PhD ya na bayani kan rashin cigaban yankin Arewa. 

A faifan da ya fito daga shafin Mahadi Shehu, an ji Dikko Radda ya na zargin son kai a matsayin abin da ya jawowa ‘Yan Arewacin Najeriya koma-baya. 
Gwamnan jihar Katsina ya amsa tambaya ne a game da abin da ya zama tarnaki da dabaibayi ga yankin duk da adadin al’umma da yawan kuri’ar zabe. 
“Hadin-kai ne, babu hadin-kai a Arewa, kowa shi kadai yake aiki. A Arewa kowa ta kan shi yake yi, babu wanda ya damu da ya al’umma za ta kasance. 
Kowa ta kan shi yake yi, babu shugabanci, babu wanda ya isa a ce shi kadai ne idan ya yi magana za a saurare shi a Arewar nan, don haka babu jagoranci. 
Saboda haka abin da mu ke bukata shi ne jagoranci, girmama manya da kuma daukar matsaya da za ta yi aiki a kan duk wani mutumin da yake a Arewa.” 
Dikko Radda ya bada misali da Yarbawa wanda ya ce idan su ka tafi Landan ko wata kasar waje, sai sun zama silar jawo ‘yanuwansa zuwa kasashen ketare. 
Exit mobile version