Home Uncategorized Gwamnonin Najeriya sun yi ta’aziyyar rasuwar ƴan Wasan Kano

Gwamnonin Najeriya sun yi ta’aziyyar rasuwar ƴan Wasan Kano

8
0

Kungiyar Gwamnonin Najeriya  ta bayyana alhini da jimami kan rasuwar wasu ‘yan wasa daga jihar Kano sakamakon mummunan hadarin mota da ya auku a ranar Asabar.

Lamarin ya faru ne a yayin da tawagar ‘yan wasan jihar ke dawowa daga gasar wasanni ta kasa da aka kammala kwanan nan a Jihar Ogun.

Shugaban Kungiyar Gwamnonin kuma gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu da kansa a yau Asabar.

“Muna mika sakon ta’aziyyarmu  ga iyalan ‘yan wasan, gwamnatin jihar, da kuma masu ruwa da tsaki a fannin wasanni a jihar Kano da Najeriya baki daya.

“Muna rokon Allah Ya jikan ‘yan wasan da suka rasu, Ya kuma ba iyalansu hakuri da juriyar wannan babban rashin,” in ji AbdulRazaq.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here