Home Uncategorized Atiku ya caccaki ‘yan majalisar wakilai kan kin amincewa da wa’adin shugaban...

Atiku ya caccaki ‘yan majalisar wakilai kan kin amincewa da wa’adin shugaban kasa na shekaru shida

7
0

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, a ranar Alhamis, ya caccaki majalisar wakilai kan kin amincewa da kudirin dokar wa’adin mulki na shekara shida ga shugaban kasa da gwamnoni.

Kudurin wanda dan majalisa mai wakiltar Ideato North/Ideato South Federal Constituency, jihar Imo, Ikenga Ugochinyere da wasu mutane 33 suka dauki nauyinsa, an yi watsi da shi ne a ranar Alhamis a wata kuri’ar da ‘yan majalisar suka kada a zauren majalisar.

A watan Oktoban shekarar da ta gabata ne Atiku ya aike da wasika ga Majalisar Dokoki ta kasa, inda ya bukaci a yi wa kundin tsarin mulki kwaskwarima domin kafa wa’adin mulki na shekara shida ga Shugaban kasa da gwamnonin jihohi.

A cikin takardar da ya mika wa kwamitin majalisar dattawa kan duba kundin tsarin mulki, Atiku ya kuma ba da shawarar a rika karba-karba a shugabancin kasa tsakanin Kudu da Arewa.

Daga Abbakar Aleeyu Anache

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here