Home Uncategorized Bagudu ya aika sunayen Shugaba da mambobin hukumar zabe ga majalisar dokokin...

Bagudu ya aika sunayen Shugaba da mambobin hukumar zabe ga majalisar dokokin jiha

7
0
Bagudu ya aika sunayen Shugaba da mambobin hukumar zabe ga majalisar dokokin jiha



 
 Gwamnan jihar Kebbi Sanata Abubakar Atiku Bagudu a ranar Talata ya aikawa majalisar dokokin jihar sunayen shugaba da mambobinsa da yake son a tantance a kuma tabbatar domin su jagoranci hukumar zabe mallakar jiha.
 
A takardar da ya  tura wadda mai baiwa gwamna shawara kan yada labarai Yahaya Sarki ya rabawa manema labarai a birnin Kebbi  ya ce sunayen sun hada da  Aliyu Muhammad Mera a matsayin shugaba, sai Ahmed Amadu Nasani, Mustapha Usman Ka’oje, Honarabul  Aliyu Ahmed Adamu da Honarabul  Sa’idu Moh’d Dankolo, dukansu mambobi ne a hukumar zaben.



Bagudu ya ce zabar mutanen yana kunshe ne a cikin daftarin doka sashe na 198 da kundin tsarin mulki wanda aka yiwa gyaran fuka a 1999.
Bagudu ya ce ya nada mutanen ne domin su taimaka masa ga hakkin da doka ta daura masa. 



 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here