Peter Obi, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar Labour (LP), ya sake bayyana niyyarsa ta shiga zaben shugaban ƙasa na shekarar 2027.
Obi ya yi wannan bayani ne yayin da yake yi wa ɗan takarar Jam’iyyar ADC kamfen a gabanin zaɓen Ƙananan hukumomi na Abuja.
Tun bayan shiga ADC, magoya bayan Obi, ciki har da ‘yan ƙungiyar Obidient, suna ƙoƙarin ganin jam’iyyar ta sanya shugabansu a saman jerin ɗan takarar shugaban ƙasa.
Sai dai, Bolaji Abdullahi, mai magana da yawun ADC, ya yi gargadi ga magoya bayan jam’iyyar game da furucin rabuwar kai, yana mai jaddada bukatar fifita haɗin kai.
Akwai jita-jita cewa wasu manyan jami’an jam’iyyar na nazarin yiwuwar haɗa Obi da Rabiu Kwankwaso a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa da mataimaki a ƙarƙashin tutar ADC.
Shawarar Kwankwaso na rashin shiga Jam’iyyar APC ya ƙara haifar da hasashe cewa haɗin Obi da Kwankwaso na iya tasowa.
Magoya bayan tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, sun kuma sake yin kira ga Obi da magoyayansa da su yi la’akari da karɓar matsayin mataimakin ɗan takara, kamar yadda aka yi a tsari na shekarar 2019.
Sai dai, Obi yaƙi irin waɗannan shawarwarin, inda ya shaida wa magoya baya cewa niyyarsa ita ce yin takara a zaben shekarar 2027 a matsayin babban ɗan takara.






