Home Daga Marubutanmu 2023:Gwamnan Adamawa Ya Nuna Rashin Gamsuwarsa Ga Takarar Tambuwal

2023:Gwamnan Adamawa Ya Nuna Rashin Gamsuwarsa Ga Takarar Tambuwal

1
0


Gwamna Umaru Fintiri na Jihar Adamawa ya bayyana goyon bayansa ga takarar tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar wajen neman shugabancin Najeriya a ƙarƙashin PDP.


Fintiri ya bayyana haka ne a wurin taron ƙaddamar da neman fitowa takarar Atiku Abubakar a ƙarƙashin PDP, wanda aka ƙaddamar ranar Laraba a Abuja.

Fintiri wanda shi ma ɗan PDP ne, ya ce Atiku ne ya fi dukkan sauran ‘yan takarar kowace jam’iyya cancantar zama shugaban ƙasa, saboda ƙwarewa da gogewarsa da irin faɗi-tashin siyasa da mulkin ƙasa da ya daɗe ya na goyayya.


Gwamnan ƙarara ya nuna rashin gansuwarsa ga takarar da takwaransa na jihar Sakkwato ke yi da kuma ganin yakamata a zaɓi wanda bai kai shekara 60 a duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here