2023:Gwamnan Adamawa Ya Nuna Rashin Gamsuwarsa Ga Takarar Tambuwal

2023:Gwamnan Adamawa Ya Nuna Rashin Gamsuwarsa Ga Takarar Tambuwal

Gwamna Umaru Fintiri na Jihar Adamawa ya bayyana goyon bayansa ga takarar tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar wajen neman shugabancin Najeriya a ƙarƙashin PDP.

Fintiri ya bayyana haka ne a wurin taron ƙaddamar da neman fitowa takarar Atiku Abubakar a ƙarƙashin PDP, wanda aka ƙaddamar ranar Laraba a Abuja.

Fintiri wanda shi ma ɗan PDP ne, ya ce Atiku ne ya fi dukkan sauran ‘yan takarar kowace jam’iyya cancantar zama shugaban ƙasa, saboda ƙwarewa da gogewarsa da irin faɗi-tashin siyasa da mulkin ƙasa da ya daɗe ya na goyayya.

Gwamnan ƙarara ya nuna rashin gansuwarsa ga takarar da takwaransa na jihar Sakkwato ke yi da kuma ganin yakamata a zaɓi wanda bai kai shekara 60 a duniya.