2023: Atiku, Saraki, Da Wike a Yanzu Su Ne Kan Gaba a Samun Tikitin PDP

2023: Atiku, Saraki, Da Wike a Yanzu Su Ne Kan Gaba a Samun Tikitin PDP

 

Jam'iyar PDP nada 'yan takarar shugban kasa 15 da kowanensu ke  son  jam'iyar ta tsayar da shi don wakiltarta a zaben 2023 dake tafe, da yawan 'yan takarar ba da gaske suke yi ba.

Sanya idanu da mayarda hankali yana kan tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da tsohon shugaban majalisar dattijai Sanata Bukola Saraki da Gwamnan jihar Revers Nyesom Wike, yayin da sauran za su cika rigarsu da iska ne a karshen tafiyar domin wasun shingo ne domin shanawa wasu kuwa da zimbar za a kai kujerar shugaban kasa a yankinsu don haka suka fito, da yawansu ba su da magoya baya a tafiyar.

 
 

Mutum 15 da za su nemi kuri'un daligate 3,700 bayan  Atiku, Saraki, Wike, akawai Bala Mohammed, Aminu Tambuwal, Mohammed Hayatou-Deen, Anyim Pius Anyim, Peter Obi, da  Sam Ohunabunwa.

Sauran su ne  Emmanuel Udom, Ayodele Fayose, Dele Momodu, Olivia Tarela, ita kadai ce mace a cikinsu, sai  Charles Okwudili, Chikwendu Kalu da Cosmos Ndukwe. Kwamitin tantancewa na Mark ya watsar da mutum biyu.

Komar da aka sanya Gwamna Aminu Waziri a cikinta bai fi ya fito daga Arewa maso Yamma ba in da tsohon shugaban kasa a jamhuriya ta biyu Alhaji Shehu Shagari ya fito, ga margayi Ummaru 'Yar'aduwa, sai yanzu kuma shugabn kasa Muhammadu Buhari nakai da wahalar gaske jam'iyar ta sake dauko wani daga yankin a 2023. 

Wata majiyar ta ce Tambuwal ya nemawa kan mafita in da ya saye fom na tkarar sanata in da ya baiwa amininsa ya rike masa waton tsohon kwamishinan filaye da gidaje na jiha Aminu Bala Bodinga, don ya yi takarar ya je majalisa ko zai samu shugaban majalisa.